An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

Jami’an hukumar tsaron farin kaya (DSS) ne suka kama ɗan ta’addan mai suna Sani Galadi, yayin da ake tantance maniyyata domin hawa jirgin zuwa ƙasar Saudiya

An kama shi ne a safiyar ranar Litinin, washegarin da jami’an tsaro suka kama wani ɗan bindiga yana yana shirin hawa mota zuwa filin jirgin sama na Abuja domin zuwa aikin Hajji.

Wani babban jami’in tsaro a Sakkwato ya shaida wa Daily Trust cewa ana yiwa Sani Galadi tambayoyi kuma yana bayar da muhimman bayanai kafin a gurfanar da shi a kotu.

Da aka tambayi jami’in yadda aka yi dan bindigar ya samu tantancewa domin zuwa aikin Hajji, ya ce “sai a tambayi hukumomin da abin ya shafa”.

Post masu alaƙa

NSCDC ta rufe wani gida da ake zargin ana safarar jarirai a Legos.

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur

‘Iran ta buɗe wa wani jirgi wuta a mashigar Hormuz