An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

Jami’an hukumar tsaron farin kaya (DSS) ne suka kama ɗan ta’addan mai suna Sani Galadi, yayin da ake tantance maniyyata domin hawa jirgin zuwa ƙasar Saudiya

An kama shi ne a safiyar ranar Litinin, washegarin da jami’an tsaro suka kama wani ɗan bindiga yana yana shirin hawa mota zuwa filin jirgin sama na Abuja domin zuwa aikin Hajji.

Wani babban jami’in tsaro a Sakkwato ya shaida wa Daily Trust cewa ana yiwa Sani Galadi tambayoyi kuma yana bayar da muhimman bayanai kafin a gurfanar da shi a kotu.

Da aka tambayi jami’in yadda aka yi dan bindigar ya samu tantancewa domin zuwa aikin Hajji, ya ce “sai a tambayi hukumomin da abin ya shafa”.

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.