Home » An Tuɓe Rawanin Soja Boy Saboda Bidiyon Baɗala

An Tuɓe Rawanin Soja Boy Saboda Bidiyon Baɗala

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda akafi saninsa da (SOJA BOY) daga sarautar Yariman Gidan Igwai dake jihar Sokoto da Masarautar ta bashi a baya.

A wata sanarwa da ta fito daga Marafan Sarkin adar, mai dauke da sa hannun Alhaji Abubakar Marafan, Masarautar ta ce ta tube rawanin Sojaboy saboda wasu dalilai da suka bayyana.

A cewar Sanarwar ‘An samu bidiyon sa yana aikata abubuwan da suka sabawa addini, al’ada da dabi’un mutanen Gidan Igwai. Bisa wannan dalili ne masarautar ta yanke hukuncin dakatarwa tare da tsige shi daga sarautarsa.

Hakazalika, Sanarwar ta bayyana irin yadda al’ummar yankin su yi tir da wannan dabi’a kuma sun nesanta kansu daga wannan abu mara kyau. Da tsohon basaraken yake aikatawa a wakokinsa.

Daga karshe masarautar tayi nasiha ga tsohon basaraken akan yaji tsoron Allah ya rungumi dabi’u irin na karantarwar addinin Musulunci.

A kwanakin baya ne hukumar tace fina-fina ta jihar Kano ta ce ta dakatar da Sojaboy saboda wasu bidiyoyi na badala da ya ke yadawa da sunan wakoki ko fina-finan Kannywood.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?