admin

Gwamnati ta maka El-Rufai a Kotu

Gwamnatin Tarayya ta maka Nasir El-Rufai, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna a kotu, kan zargin kutsen intanet a layin sadarwar Mashawarcin Shugaban Kasa kan sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu. Hukumar Tsaro ta DSS ce ta shigar da kara gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda take tuhumar El-Rufai da laifuka uku masu alaka da kutsen intanet. […]

Read more

DSS ta kama wanda ya sace yaro dan shekara 5 a Kano

Hukumar  tsaron ta farin kaya (DSS) ta samu nasarar ceto wani yaro mai shekaru biyar, mai suna Muhammad Haruna, daga hannun masu garkuwa da mutane a Kauyen Danzaki, karamar hukumar Gezawa. An gudanar da aikin ceton ne da misalin ƙarfe 7:40 na yamma ranar Alhamis, bayan an sami rahoton cewa an sace yaron kuma masu […]

Read more

Yadda Aka Karrama Janar Murtala Muhammed A Abuja

Manyan mutane sun hallara a Abuja, a ranar Juma’a, domin tunawa da cika shekaru 50 da kisan tsohon Shugaban ƙasa, Janar Murtala Muhammed. An kashe marigayi Janar ne tare da wasu muƙarrabansa, a wani yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba a Legas, ranar 13 ga Fabrairu, 1976. Jami’an rundunar sojin Najeriya sun yi […]

Read more

Ana Fargabar Ɓullar Zazzaɓin Lassa A Gombe

An samu rahoton wasu mutane huɗu da ake zargin sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa a Jihar Gombe, sa’o’i kaɗan kafin ƙaddamar da shirin ‘Ranar Ba Da Gudunmawar Jini’  wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar. Majiyoyi daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Gombe sun bayyana cewa, daga cikin mutanen huɗun da ake zargin har da […]

Read more