Ana Fargabar Ɓullar Zazzaɓin Lassa A Gombe

An samu rahoton wasu mutane huɗu da ake zargin sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa a Jihar Gombe, sa’o’i kaɗan kafin ƙaddamar da shirin ‘Ranar Ba Da Gudunmawar Jini’  wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar.

Majiyoyi daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Gombe sun bayyana cewa, daga cikin mutanen huɗun da ake zargin har da matar wani tsohon Kwamishina da kuma wasu mutum uku.

A halin yanzu, ana tsare da marasa lafiyar domin kulawa ta musamman yayin da hukumomin lafiya ke ƙara ƙaimi wajen tabbatar da sahihancin zargin ta hanyar gwaje-gwaje a ɗakin bincike.

Wata majiya da ba ta bayyana sunanta ba ta kuma nuna damuwa kan ƙarancin magunguna, inda ta ce allurai guda biyu ne kawai ake da su a halin yanzu, kuma wasu daga cikin magungunan ma sun riga sun ƙare wa’adinsu.

Sai dai har yanzu hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance domin tabbatar ko musanta waɗannan zarge-zarge ba.

Dangane da wannan lamari, ana shirin buɗe cibiyar killace marasa lafiya a Kwadon domin kula da waɗanda ake zargi da cutar tare da hana yaɗuwarta zuwa sauran al’umma.

Post masu alaƙa

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Tinubu ya nemi kotu a Amurka ta hana fitar da takardun zarginsa da safarar ƙwaya’

Sauron da jirgin sama ya ɗauko daga Afirka sun yi ajalin mutane 2 a Jamus