Bam Ya Sake Tashi A Zamfara Cikin Sati Guda A Karo Na 3

Wasu bama-bamai guda biyu sun tashi a wasu wurare a gundumar Dansadau da ke karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Jaridar PremiumTimes ta ruwaito cewa, bama-baman biyu sun fashe ne akan titin Dansadau zuwa Malamawa dayan kuma a kan titin Malele, duk a gundumar Dansadau.

Wani mazaunin yankin da abin ya faru Nuhu Babangida ya ce wata motar fasinja ce da ke kan hanyar kasuwar mako-mako ta Dansadau a safiyar Juma’a ta taka bam din.

Babangida ya ce bama-baman da suka fashe a kan titin Malamawa da Malele sun tashi ne a lokaci guda amma ba a samu asarar rai ba.

Wannan dai shine karo na uku da bam ya tashi a jihar Zamfara, kuma an dora alhakin tada bama-baman akan ‘yan ta’addar lakurawa.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya