An Sace Motar Malam Nuhu Ribadu

Wasu da ake zargin ɓarayi ne sun sace motar ofishin Malam Nuhu Ribadu, mai bai wa shugaban ƙasa shawara a fannin tsaro a wani masallacin juma’a dake birnin tarayya Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa an ajiye motar a kusa da wani masallacin birnin tarayya Abuja da misalin ƙarfe 1:05, lokacin da jami’an ofishin Nuhu Ribadu suka je yin sallar juma’a.

Tuni dai jami’an rundunar ƴan sandan Abuja suka fara gudanar da binciken wadanda suka sace motar mai ƙirar Toyota Hilux.

Rahotanni sun bayyana cewa  jami’an ofishin na Ribadu sun iske babu motar a wajen da suka ajiye ta yayin da suka kammala Sallar Juma’ar

Post masu alaƙa

Ana zargin mahaifi da kashe ’yarsa kan auren dole a Katsina

An kama mutum 2 kan zargin sayar da filayen gwamnatin a Kano

Waɗanda suka sace ɗaliban Oyo sun buƙaci musaya da manyansu muka ƙi’