Kwararren lauyan, Barista Hamza Nuhu Ɗantani ya yabawa kwamishinonin yan sanda uku kan ƙwarewa da jajircewa wajen tabbatar da doka
Kwararren lauyanan, Barista Hamza Nuhu Ɗantani, ya yaba wa kwamishinonin yan sanda uku bisa abin da ya bayyana a matsayin ƙwarewa da rikon amana da jajircewa wajen tabbatar da bin doka da oda, da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Kwamishinonin da ya yaba wa sun haɗa da kwamishinan yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori da kwamishinan babban birnin tarayya , CP Ahmed Muhammed Sunusi da kuma kwamishinan yan sanda na jihar Borno, CP Naziru Abdulmajid.
Barista Ɗantani ya ce, ya ce kwamishinonin yan sandan suna gudanar da aiyukansu bisa kwarewa da gaskiya da adalci kuma sauke nauyin da aka ɗora na tabbatar tsaro.
Ya bayyana cewa jami’an na ci gaba da nuna jajircewa wajen tabbatar da bin doka, wanzar da zaman lafiya, kare lafiyar al’umma da dukiyoyinsu, tare da gudanar da aiyukansu bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Najeriya da ƙa’idojin aikin rundunar yan sandan kasar.
A cewarsa, ko da yake babu wata hukuma da ba ta fuskantar ƙalubale, yana da matuƙar muhimmanci a riƙa yaba wa mutanen da ke gudanar da aiyukansu cikin ƙwarewa, adalci da mutunta doka.
Barista Hamza Nuhu ya kuma bayyana fatansa cewa sauran kwamishinonin yan sanda a sassa daban-daban na ƙasar za su yi koyi da irin wannan salon jagoranci da ke fifita gaskiya, ƙwarewa, ɗaukar nauyi da mutunta doka.
