Mai Shari’a Zainab Bulkachuwa Ta Musanta Batun da Mijinta Ya Yi Kan Yin Alfarma
Tsohuwar Shugabar Kotun Daukaka Kara ta Najeriya Mai Shari’a Zainab Bulkachuwa ta musanta kalaman da mai gidanta ya yi na cewa ya yi amfani da damarsa, wajen nema wa abokan siyasarsa Sanatoci alfarma lokacin da take aiki a matsayin alkaliya.