Labarai

Babban Labari

Gwamnan Bauchi Na Shirin Sauya Sheka Zuwa ADC

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana shirinsa na sauya sheka zuwa Jam’iyyar ADC, inda ya ce jam’iyyar na da damar kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2027. Idan Bala Mohammed ya sauya shekar, ADC ta samu gwamna mai ci na farko, wanda hakan zai kara mata karfi a kan tsofaffin gwamnoni da tsofaffin […]

Babban Labari

Ƴan majalisar wakilai 8 na Kano sun fice daga NNPP zuwa APC

Ƴan Majalisar Wakilai takwas daga Jihar Kano sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar NPP zuwa jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara girgiza siyasar jihar. Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya sanar da sauya sheƙar a hukumance yayin zaman majalisar a yau Talata, bayan karanta wasiƙun da ‘yan majalisar suka aike wa zauren. A cikin […]

Babban Labari

NOA ta ƙaddamar da manhajar ClheeanMobile App don ƙarfafa hulɗa tsakanin gwamnati da jama’a

Hukumar wayar da kan jama’a ta ƙasa (NOA) ta ƙaddamar da wata sabuwar manhajar waya mai suna CLHEEAN Mobile App, wadda aka tsara domin ƙarfafa hulɗa tsakanin gwamnati da al’umma tare da rage gibi a harkokin mulki. Daraktan Janar na hukumar, Malam Lanre Issa-Onilu, ya bayyana cewa manhajar za ta bai wa ‘yan Najeriya damar […]

Babban Labari

El-Rufai ya sake gurfana a kotun Kaduna

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya sake gurfana a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna a ranar Talata kan tuhumomin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC) ta shigar a kansa. An gurfanar da El-rufai ne kan laifuka da suka hada da amfani da mukami ba bisa ka’ida ba, damfara, da bai wa […]

Babban Labari

Komawar Kwankwaso ADC barazana ce ga APC

Mai fashin baƙi akan al’amuran yau da kullum a Nijeriya, Ibrahim Sadauki Kabara, ya bayyana cewa komawar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, jam’iyar ADC babbar barazana ce ga jam’iyyar APC a Kano dama ƙasa baki ɗaya. Komawar Kwankwaso, wanda shi ne tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, […]

Babban Labari

Kwankwaso ya koma jam’iyyar ADC tare da magoya bayansa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso ya koma jam’iyyar haɗaka ta ADC tare da magoya bayansa bayan ficewarsa daga jam’iyyar NNPP. An gudanar da bikin komawarsa ne a gidansa da ke Kano, inda shuwagabannin jam’iyyar da dimbin magoya bayansa suka hallara domin tarbar sa. Tsohon gwamnan ya kuma buƙaci magoya bayansa […]

Babban Labari

PDP tsagin Wike ta zaɓi sabbin shugabanninta

Jam’iyyar PDP tsagin Mininstan Abuja, Nyesom Wike ta zaɓi Abdulrahman Mohammed a matsayin sabon shugabanta na ƙasa yayin da Samuel Anyanwu ya samu matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa. Mohammed da Anyanwu sun samu kujerunsu ta hanyar masalaha, tare da sauran mambobin kwamitocin jam’iyyar ta ƙasa guda 19 a babban taron jam’iyyar na shekarar 2026 da […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000