Labarai

Babban Labari

INEC ta yi watsi da kiraye-kirayen cire shugabanta

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi watsi da kiraye-kirayen da wasu ke yi wa shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan ya sauka daga muƙaminsa. Cikin wata sanarwa da INEC ɗin ta fitar ta bayayna kiraye-kirayen da hari kan dokokin da suka kafa hukumar. A ranar Alhamis ne jam’iyyar ADC mai hamayya a ƙasar, ɓangaren David Mark ta […]

Babban Labari

Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano CP Ibrahim Adamu Bakori ya raba tallafin ₦8,431,768.80 ga iyalan yan sandan da suka rasu.

Rundunar ‘ƴan sandan Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin , CP Ibrahim Adamu Bakori,  ta raba Cek ɗin kuɗi Naira miliyan takwas da dubu ɗari 431 da 768 da kobo 80 (₦8,431,768.80) ga iyalan jami’an rundunar 18 da suka rasu. Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar CSP Abdullahhi Haruna Kiyawa, ya bayyana ta cikin wata […]

Babban Labari

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta tattauna da ƙungiyoyi don magance tada tarzoma a lokutan zaɓe.

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta gana da ƙungiyoyin farar hula (CSOs) domin tattauna hanyoyin hana tashin hankali a lokutan zaɓe, a wani ɓangare na bikin ranar ƴan sandan Nijeriya ta shekarar 2026. Sanarwar da kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar ya ce kwamishinan ƴan sandan jihar, CP Ibrahim […]

Babban Labari

Tinubu ya gana da shugaban Chadi

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙucnin shugaban Chadi Idriss Déby a ranar Alhamis. Sun yi ganawar ce cikin sirri a fadar shugaban Najeriya da ke Abuja, inda ake sa ran sun tattauna kan batutuwa da suka shafi tattalin arziki da kuma haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu. Ganawar na zuwa ne kafin tafiyar shugaba […]

Babban Labari

Rundunar ƴan sandan Nijeriya shiya ta ɗaya ta buƙaci jama’a su kaucewa tada tarzoma lokacin zaɓe.

Rundunar ƴan sandan Nijeriya shiya ta ɗaya dake Kano, ta buƙaci jama’a su kasance masu kaucewa dukkan wani abu da zai tayar da tarzoma lokacin gudanar da zaɓe. Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan shiyar, DSP Abdullahi Hussaini, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai. Wannan na zuwa […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000