• Home  
  • CBN: Majalisar Dattawa ta shiga karatu na II kan ƙudurin shiga siyasar ma’aikata
- Labarai

CBN: Majalisar Dattawa ta shiga karatu na II kan ƙudurin shiga siyasar ma’aikata

A jiya Majalisar Dattawa ta kammala karatu na biyu na ƙuduri wanda ya shafi babban bankin ƙasar nan, inda aka buƙaci a yi doka da za ta hana duk wani gwaman bankin da ke bakin aiki shiga harkokin siyasa.

CBN: Majalisar Dattawa ta shiga karatu na II kan ƙudurin shiga siyasar ma'aikata

A jiya Majalisar Dattawa ta kammala karatu na biyu na ƙuduri wanda ya shafi babban bankin ƙasar nan, inda aka buƙaci a yi doka da za ta hana duk wani gwaman bankin da ke bakin aiki shiga harkokin siyasa.

Sanata mai wakiltar Yammacin jihar Kogi, sanata Steve Karimi na jam’iyyar APC, ne ya gabatar da ƙudurin, sai kuma makamancin wannan ƙuduri da sanata mai wakiltar jihar Abia ta tsakiya na jam’iyyar LP, shi ma ya gabatar.

A baya-bayan nan an ga yadda tsohon gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele, ya shiga siyasa da ta kai ga neman takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar APC a lokacin da yake kan aiki wanda hakan ya jawo cece-ku-ce.

Sanata Karimi ya bayyana cewa, manufar wannan ƙuduri shi ne tabbatar da an tafi da harkokin babban banki yadda ya kamata tare da haramta amfani da kuɗaɗen ƙetare a yayin kasuwanci na cikin gida.
Sannan ya buƙaci a sake duba sashe na 9(2) na kundin CBN wanda ya buƙaci a haramta wa gwamnan babban banki da mataimakinsa shiga harkokin siyasa da neman kowacce irin takara a lokacin da suke riƙe da ofisoshin gwamnati.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai