Home » Dakta Bashir Ya Zama Shugaban  Asuu Na Jami’ar Ilimi Ta Kano

Dakta Bashir Ya Zama Shugaban  Asuu Na Jami’ar Ilimi Ta Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Rumasau Muhammad Idris

A karon farko, malaman Jami’ar Ilimi ta Tarayya dake kano sun kaddadamar da sabuwar kungiyar ASUU.

Wannan na kun she a cikin wata  takardar bayan taron  da  a ka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun shugaban taron Abdulkarim Ahmad Tijjani.

A yayin taron, an cinma matsayar shugabancin kungiyar,  inda mahalarta taron suka zabi Dakta Bashir ibrahim a matsayin shugaba.

Yayin da aka zabi Dokta Aliyu Yaya Aliyu amatsayin sakatare da kuma sauran masu taimakusu kamar yadda sanarwa ta bayyana.

Haka kuma an cinma matsaya akan wasu bukatun malaman jami’ar, inda aka mika su ga  gajorancin makarantar domin tunkarar kalubalen da ke fuskantar su.

Daga karshe an yanke shawayar gayyatar sauran malaman jami’ar dake sha awar shiga kungiyar domin zama manbobi tare da yunkurin samarda kundin tsarin da fiyar da kungiya,

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?