Dubun masu ƙera muggan makamai a Filato ta cika

Dubun wasu masu ƙera muggan makamai ta cika a yankin Lantang da ke Jihar Filato mai yawan fama da rikice-rikice da hare-hare.

Sojojin Rundunar Operation Enduring Peace sun kama manyan bindigogi uku, ƙirar AK-47 guda biyu da kuma ƙirar G3 guda ɗaya a hannun masu ƙera makamai ba bisa ka’ida ba.

Mutanen sun shiga hannun sojoji ne a lokacin da dakarun rundunar suka kai samame a masana’antar makaman da ke yankin Gwandanu, da ke ƙaramar hukumar Langtang.

Kakakin rundunar, Kyaftin Polycarp Oteh, ya ce sojojin sun kama mutanen tare da kayan aikinsu ne, a yayin da suke tsaka da aikin ƙera muggan makaman.

Post masu alaƙa

Dalilin da ya sa na gina Masallatai 50 da aurar da marayu 10 — Mataimakin Gwamna

Dalilin da ya sa zan yi takara – Yusuf Buhari

An tsinci gawar matashi a kusa Asibitin Mallam Aminu Kano.