Daga : Sharif Khalifa Sharifai
Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana ranar Alhamis, 26 ga Yuni, 2025 a matsayin ranar hutun murnar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 bayan Hijira.
Wannan na cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar a ranar Laraba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya taya al’ummar Musulmi murnar samun damar ganin sabuwar shekara, wadda ke farawa da watan Muharram – watan farko a kalandar Musulunci.
- An Yankewa Masu Satar Yara A Kano Hukuncin Shekaru 120
- Wata Babbar Kotun Tarayya Ta Yankewa Yan Chaina Shida Hukunci.
Ya kuma bukaci jama’a da su yi nazarin abubuwan da suka gabata tare da amfani da wannan dama wajen yin addu’ar neman zaman lafiya, hadin kai da ci gaban Kano da Najeriya gaba ɗaya.