Gobe Ba Aiki A Kano: Hutun Sabuwar Shekarar Musulunci 1447

Daga : Sharif Khalifa Sharifai

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana ranar Alhamis, 26 ga Yuni, 2025 a matsayin ranar hutun murnar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 bayan Hijira.

Wannan na cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar a ranar Laraba.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya taya al’ummar Musulmi murnar samun damar ganin sabuwar shekara, wadda ke farawa da watan Muharram – watan farko a kalandar Musulunci.

Ya kuma bukaci jama’a da su yi nazarin abubuwan da suka gabata tare da amfani da wannan dama wajen yin addu’ar neman zaman lafiya, hadin kai da ci gaban Kano da Najeriya gaba ɗaya.

Post masu alaƙa

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC

DSS ta kama mutane 5 da ake zargi da sace ɗaliban makarantar St. Mary’s Pipiri a jihar Neja