Home » Gwamna Abba Ya Kirkiro Sabbin Hukumomi 4 A Kano

Gwamna Abba Ya Kirkiro Sabbin Hukumomi 4 A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Kano na daura auren zaurawa a yau

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rattaba hannu kan wasu dokoki  guda huɗu domin kafa sabbin hukumomi a jihar.

Dokokin da ya sanya wa hannu za su samar da Hukumar Kare Hakkokin Jama’a ta Jihar Kano (KASPA), da Hukumar Kula da Tallace-tallace da Rubuce-rubuce ta Jihar Kano (KASIAA), da Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa da Zamani ta Jihar Kano (KASITDA), da kuma Hukumar Bunƙasa Ƙananan Kasuwanci da Matsakaita ta Jihar Kano (KASMEDA).

Mai magana da yawun gwamanan Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana muhimmancin waɗannan dokokin wajen ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire, tallafa wa ƙananan kasuwanci, tsara tallace-tallace, inganta kare hakkin jama’a da samar da ayyuka.

Sanusi Bature ya kara da cewa an yi wadannan dokokin ne domin ƙarfafa tsarin gudanarwa na jihar da kuma haɓaka ci gaba mai ɗorewa.

Gwamnan ya jaddada cewa waɗannan hukumomi za su taka muhimmiyar rawa wajen samar da ayyukan yi, da kuma aiwatar da tsare-tsaren gwamnati yadda ya kamata.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?