Home » Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya rantsar da sabbin kwamishinoni 35

Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya rantsar da sabbin kwamishinoni 35

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya rantsar da sabbin kwamishinoni 35

Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya rantsar da sabbin kwamishinoni akalla 35 da ya naɗa a matsayin mambobin majalisar zartarwasa.

Sabbin kwamishinonin sun yi rantsuwar kama aiki ne a zauren majalisar zartarwa da ke fadar gwamnatin jihar Ebonyi, inda Gwamnan ya buƙace su da su kawo sabbin abubuwa da dabarun sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

Haka nan kuma gwamna Nwifuru ya rantsar da shugaban ma’aikatansa, Farfesa Emmanuel Echiegu, da mataimakinsa, Injiniya Timothy Nwachi, da mashawarta na musamman da sauransu.

Da yake jawabi ga waɗanda ya bai wa mukamai, gwamnan ya ce ya naɗa su muƙamai ne ba dan siyasa ba, inda ya roƙesu da su haɗa hannu wuri ɗaya domin kai jihar tudun mun tsira, ya kuma ce gwamnatinsa ba zata lamurci sakarci ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?