Home » Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya kafa kwamitin kwato kadarorin jihar

Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya kafa kwamitin kwato kadarorin jihar

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya kafa kwamitin kwato kadarorin jihar

Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya kafa kwamiti da zai yi duba da kuma ƙwato kadaron jihar a faɗin Najeriya.

An ɗora wa kwamitin alhakin bincikowa da kuma gano kadarori a jihar Kaduna da ofishin jihar ta Taraba da ke Legas da kuma Abuja, babban birnin Tarayya.

A cewar sanarwar da Sakataren Gwamnatin Jihar Gebon Kataps ya fitar , ya ce an ɗora wa kwamitin nauyin nema da kuma gano inda kowane irin nau’in kadarorin gwamnatin suke a faɗin ƙasar nan.

Ya ce kwamitin zai kuma duba ƙimar kuɗin kowace kadara da kuma bai wa gwamnatin jihar shawarwari.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin makonni huɗu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?