Home » Gwamnan Kano Ya Buƙaci NBC Ta Sa Ido Kan Kafofin Yaɗa Labarai Na Intanet

Gwamnan Kano Ya Buƙaci NBC Ta Sa Ido Kan Kafofin Yaɗa Labarai Na Intanet

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga hukumar kula da kafafen yaɗa labarai a Najeriya NBC ta da fara kula da ayyukan kafofin rediyo da talabijin na intanet.

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment
Gwamnatin Kano Ta Nada Laminu Rabiu Sabon Sakataren Hukumar Alhazai

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga hukumar kula da kafafen yaɗa labarai a Najeriya NBC ta da fara kula da ayyukan kafofin rediyo da talabijin na intanet.

Gwamnan ya ce sanya ido kan abubuwan da kafofin suke yaɗawa a intanet zai taimaka wajen daƙile yaɗa labaran bogi da ma abubuwan da za su iya tayar da zaune tsaye.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren watsa labaran gwamnan, Mustapha Muhammad ya fitar daga cikin tsakuren jawabin da gwamnan ya gabatar a taron ƙara wa juna sani da Hukumar NBC ta shirya a jihar Legas.

A jawabinsa, gwamnan wanda ya samu wakilcin darakta-janar harkokin watsa labarai da hulɗa da jama’a, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya nuna takaicinsa kan yadda ake abin da aka ga dama a amfani da intanet wajen yaɗa abubuwan da ba su dace, “wajen yaɗa abubuwan da suke jawo rarrabuwar kai musamman na addini da siyasa. Yanzu saboda rashin sa ido, intanet ya zama wajen baje-kolin labaran bogi da kalaman ɓatanci.”

Ya ce lokaci ya yi da NBC za ta fara kula da ayyukan kafofin da suke yaɗa labarai ta intanet domin tsabtace abubuwan da suke yaɗawa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?