Gwamnan Kano ya umarci kwamishinonin da zai nada da su bayyana dukiyarsu kafin kama aiki

Taswirar Jihar Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya umarci dukkan kwamishinoni da ya naɗa da su hanzarta yin biyayya ga dokoki da ƙa’idojin aiki wanda suka zama tilas.

 Inda yaƙara da cewar, daga yanzu, duk wanda ya san sunansa ya shiga cikin waɗanda za’a naɗa kwamishina ya bayyana dukiyar da ya mallaka gabanin majalisa ta tantance shi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wata gajeruwar sanarwa da gwamnatin Kano ta fitar a yau Laraba, inda gwamnan ya sha alwashin cewa duk kwamishinan da ya kauce wa cike Fam din bayyana dukiya daga hukumar kula da ƙa’idojin aiki, ba zai rantsar da shi ba.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudurinsa ga al’ummar jihar Kano, inda ya ce, gaskiya da kiyaye haƙƙin sauke nauyi ne zasu zama alkiblar gwamnatinsa.

A cewarsa, ta haka ne kaɗai zai cika alkawarin da ya ɗauka a kakar zaɓe da kuma abinda ke cikin kundin manufofinsa na kafa nagartacciyar gwamnati da kowa zai yi na’am da ita.

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro