Gwamnan Zamfara ya yi naɗe-naɗen farko na hidimansa

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya yi naɗe-naɗen farko na waɗanda za su taimaka masa wajen tafiyar da gwamnati.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abubakar Nakwada ne ya sanar da haka a wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Hakokin Kafafan sadarwa na zamani ga Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya sanya wa hannu kuma ya raba wa manema labarai a Gusau babban burnin jihar.

 Sulaiman ya ce, gwamnan ya naɗa Alhaji Abubakar Nakwada a matsayin sakataren gwamnatin jihar. Haka kuma ya naɗa Mukhtar Lugga a matsayin Shugaban Ma’aikata.

Gwamnan Jihar, ya kuma amince da naɗin Sharifudden F. Jatto a matsayin Babban Sakataren Gwamna; sai Imran Rufa’i Ahmad, a matsayin Mataimaki na Musamman ga Gwamna.

Yayinda Ali Akilu Bungudu ya zama babban mataimaki na musamman kan harkokin tattalin arziki.

Post masu alaƙa

Atiku ya buƙaci Tinubu ya yi bayanin dalilinsa na ƙin halartar taron UNGA karo na uku a jere

Yan sanda da INEC sun yaba da yadda zaɓen Dawakin Kudu ke gudana a Kano.

An dakatar da shugaban NSCDC a Neja kan mutuwar masu haƙar ma’adanai 37