Gwamnatin Jihar Adamawa ta sanya dokar hana zirgazirga ta awanni 24

RAHOTO: Hassan Umar Shamfella, Adamawa.

Gwamnatin jihar Adamawa ƙarƙashin jagorancin Ahmadu Umaru Fintiri, ta saka dokar hana fita ta tsawon awowi 24, a faɗin jihar, biyo bayan farfasa wuraren ajiyar abinci da matasa suka yi.

Mai magana da yawun hukumar ‘yan sandan jihar Adamawa ya ƙara da cewa i zuwa yanzu an kama mutane 44, kuma an ƙwato sauran kayayyakin da aka sace.

Har wa yau kuma mun jiyo ra’ayoyin wasu mazauna garin na Yola dangane da wannan al’amari da ya faru.

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro