Home » Gwamnatin Jihar Legas Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Kwalara A Gidan Yarin Kirikiri 

Gwamnatin Jihar Legas Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Kwalara A Gidan Yarin Kirikiri 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
kirikiri

Mako guda bayan hukumar kula da gidajen yarin Najeriya  ta bayyana cewa babu ɓullar cutar kwalara a cibiyoyinta da ke fadin kasar nan,  kwamishinan lafiya na jihar Legas ya bayyana cewa an samu mutum 25 da suka kamu da kwalara a gidan yari na Kirkiri da ke jihar.

Darakatan yada labarai na ma’aikatar lafiya ta jihar Legas, Tunbosun Ogunbanwo ne ya bayyana hakan in da ya ce,  kawo yanzu mutane 25 ne  suka koka kan mummunan ciwon ciki.

Sanarwar ta ce, an ɗauki matakin gaggawa wajen shawo kan lamarin.

Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya ta ce mutum 53 ne suka mutu a watan Yunin 2024 sanadiyyar yaɗuwar cutar a faɗin ƙasar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?