• Home  
  • Gwamnatin Jihar Legas Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Kwalara A Gidan Yarin Kirikiri 
- Babban Labari - Labarai

Gwamnatin Jihar Legas Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Kwalara A Gidan Yarin Kirikiri 

Mako guda bayan hukumar kula da gidajen yarin Najeriya  ta bayyana cewa babu ɓullar cutar kwalara a cibiyoyinta da ke fadin kasar nan,  kwamishinan lafiya na jihar Legas ya bayyana cewa an samu mutum 25 da suka kamu da kwalara a gidan yari na Kirkiri da ke jihar. Darakatan yada labarai na ma’aikatar lafiya ta […]

kirikiri

Mako guda bayan hukumar kula da gidajen yarin Najeriya  ta bayyana cewa babu ɓullar cutar kwalara a cibiyoyinta da ke fadin kasar nan,  kwamishinan lafiya na jihar Legas ya bayyana cewa an samu mutum 25 da suka kamu da kwalara a gidan yari na Kirkiri da ke jihar.

Darakatan yada labarai na ma’aikatar lafiya ta jihar Legas, Tunbosun Ogunbanwo ne ya bayyana hakan in da ya ce,  kawo yanzu mutane 25 ne  suka koka kan mummunan ciwon ciki.

Sanarwar ta ce, an ɗauki matakin gaggawa wajen shawo kan lamarin.

Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya ta ce mutum 53 ne suka mutu a watan Yunin 2024 sanadiyyar yaɗuwar cutar a faɗin ƙasar.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai