Home » Daukar nauyin ilimi ya fi karfin gwamnatin Tarayya-Ministan Ilimi na Najeriya

Daukar nauyin ilimi ya fi karfin gwamnatin Tarayya-Ministan Ilimi na Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Tahir Mamman

Ministan Ilimi, farfesa Tahir Mamman, ya ce gwamnatin tarayya kadai ba za ta iya daukar nauyin ilimi ba a kasar nan.

Ministan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron karramawa da aka shirya wa Dr. Emeka Offor da matarsa, Adaora Offor wadanda jami’ar Nsukka da jami’ar Nnamdi Azikiwe suka ba wa digirin girmamawa a kan fanin kasuwanci da fafutukar al’umma.

Ministan ya kara da cewa, gwamnati tana kashe kudade masu yawan gaske wajen daukar nauyin makarantu, inda ya ce akwai bukatar shigowar makarantu masu zaman kansu da kuma masu ba da taimako domin ganin an ciyar da ilimi gaba kamar yadda gidauniyar mista Offor ke yi.

Ya ce wannan zai karfafa wa gwamnati domin ba za ta iya daukar nauyin ilimi ba ita kadai ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?