• Home  
  • Gwamnatin Borno Ta Ce ‘Yan Boko Haram Ne Suka Kai Hari Gwoza
- Babban Labari - Labarai

Gwamnatin Borno Ta Ce ‘Yan Boko Haram Ne Suka Kai Hari Gwoza

Gwamnatin jihar Borno ta dora alhakin harin kunar bakin wake da aka kai kan masu daurin aure a garin Gwoza kan mayakan Boko Haram. Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Borno, Usman Tar, ya shaida wa manema labarai cewa kungiyar masu tada kayar baya ta Boko Haram ce ta kai harin.  Ya ce ‘yan ta’addar […]

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum

Gwamnatin jihar Borno ta dora alhakin harin kunar bakin wake da aka kai kan masu daurin aure a garin Gwoza kan mayakan Boko Haram.

Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Borno, Usman Tar, ya shaida wa manema labarai cewa kungiyar masu tada kayar baya ta Boko Haram ce ta kai harin. 

Ya ce ‘yan ta’addar sun kai wannan hari ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke shirin mayar da mazauna yankunan gidajensu da ke gudun hijira a halin yanzu.

Gwamnatin jihar ta ce, tana shirin rufe sansanin ‘yan gudun hijira da ke jihar baki daya daga nan zuwa shekarar 2026.

Usman Tar ya ce  harin na ranar asabar din karshen makon da ya gabata  da ya hallaka mutune 18 bai musu dadi ba. 

 

 

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000