Home » Gwamnatin Borno Ta Ce ‘Yan Boko Haram Ne Suka Kai Hari Gwoza

Gwamnatin Borno Ta Ce ‘Yan Boko Haram Ne Suka Kai Hari Gwoza

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum

Gwamnatin jihar Borno ta dora alhakin harin kunar bakin wake da aka kai kan masu daurin aure a garin Gwoza kan mayakan Boko Haram.

Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Borno, Usman Tar, ya shaida wa manema labarai cewa kungiyar masu tada kayar baya ta Boko Haram ce ta kai harin. 

Ya ce ‘yan ta’addar sun kai wannan hari ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke shirin mayar da mazauna yankunan gidajensu da ke gudun hijira a halin yanzu.

Gwamnatin jihar ta ce, tana shirin rufe sansanin ‘yan gudun hijira da ke jihar baki daya daga nan zuwa shekarar 2026.

Usman Tar ya ce  harin na ranar asabar din karshen makon da ya gabata  da ya hallaka mutune 18 bai musu dadi ba. 

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?