Home » Gwamnatin Kamaru Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 4 A Zanga-zangar Da Ake Ci Gaba Da Yi.

Gwamnatin Kamaru Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 4 A Zanga-zangar Da Ake Ci Gaba Da Yi.

Gwamnatin Kamaru ta tabbatar da cewa mutum hudu suka mutu a zanga-zangar da ƴanƙasar suka gudanar a ranar Lahadi a birnin Doula gabanin sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙa

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Gwamnatin Kamaru ta tabbatar da cewa mutum hudu suka mutu a zanga-zangar da ƴanƙasar suka gudanar a ranar Lahadi a birnin Doula gabanin sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a yau Litinin.

Ɗaruruwan magoya bayan ɗantakarar adawa, Issa Tchiroma Bakari ne suka fito zanga-zangar.

Tchiroma Bakary ya ƙalubalanci shugaba Paul Biya – wanda ya shafe shekara 43 yana shugabanci a ƙasar.

Tuni jagoran adawar ya ayyana cewa shi ne ya yi nasara a zaɓen, duk da cewa a yau Litinin ne ake sa ran sanar da sakamakon a hukumance.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?