• Home  
  • Kasashen Mali, Burkina Faso, Nijar sun fice daga ECOWAS
- Labarai

Kasashen Mali, Burkina Faso, Nijar sun fice daga ECOWAS

Ƙasar Mali a maimakon ƙasashen Burkina Faso da Nijar, ta rubuta wa ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma, wato ECOWAS, takardar sanarwa na ficewa daga ƙungiyar nan take. ƙasashen sun zargi ƙungiyar da sauka daga manufofin da suka assasa kafa ƙungiyar waɗanda ke ƙunshe da aƙidar bunƙasa yankin Afirka. Sannan sun zargi ECOWAS […]

MALI

Ƙasar Mali a maimakon ƙasashen Burkina Faso da Nijar, ta rubuta wa ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma, wato ECOWAS, takardar sanarwa na ficewa daga ƙungiyar nan take.

ƙasashen sun zargi ƙungiyar da sauka daga manufofin da suka assasa kafa ƙungiyar waɗanda ke ƙunshe da aƙidar bunƙasa yankin Afirka.

MALI
Sannan sun zargi ECOWAS da mara wa manufofin Turawan Yamma baya wanda kuma hakan barazana ne ga ƙasashen biyu a cewar takardar sanarwar.

Wannan mataki na nuna yankewar alaƙar ƙasashen na shekaru 49 tun bayan kafa ƙungiyar a ranar 28 ga watan Mayun shekarar 1975.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai