Gwamnatin Najeriya Na Shirin Samar da Tallafin Ga Al’umma Bayan Cire Tallafin Mai

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci majalisar Kan Tattalin Arzikin Kasa NEC, a karkashin Kashim Shettima, ta fito da yadda za a rage radadin cire tallafin fetur ga al’uma.

Gwamnan jihar Ogun, Dapo Abiodun ne ya bayyana haka a jiya Laraba bayan shugaban Kasa ya zauna da manyan ‘yan kasuwan mai a fadar Aso Rock.

Abiodun wanda ya taba zama shugaban kungiyar ‘yan kasuwan na mai, ya ce ‘yan kasuwa sun nuna goyon bayan cire tallafin fetur da Bola Tinubu ya yi.

Haka kuma rahoton ya ce ‘yan kasuwan sun yi alkawarin bada gudumuwar manyan motocin daukar mutane 50 zuwa 100 domin a taimakawa talakawa.

Sun ce Kowace mota ta kai kusan Naira miliyan 100, saboda haka za a kashe kimanin N10bn a sayen

Rahotan yayi nuni da cewar, majalisar da ke kula da tattalin arzikin za ta yi nazarin karin mafi karancin albashi.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr