Home » Gwamnatin Najeriya za ta rage kashi 20% na magungunan da ake shigo da su kasar nan

Gwamnatin Najeriya za ta rage kashi 20% na magungunan da ake shigo da su kasar nan

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Najeriya za ta rage kashi 20% na magungunan da ake shigo da su kasar nan

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta rage shigo da magunguna cikin ƙasar daga kashi 60 zuwa kashi 40 cikin 100 domin bunkasa harkar sarrafa magunguna a cikin gida.

Mai bai wa shugaban kasa shawara ta musamman kan harkar lafiya, Salma Anas-Ibrahim ce ta bayyana hakan a wani taron ƙarawa juna sani da aka shirya domin karfafa dabarun hadin gwiwa tsakanin Hukumar Lafiya ta Duniya a Abuja.

A cewarta, wannan wani ɓangare ne na burin da Shugaba Bola Tinubu ya sanya gaba da nufin cike giɓin da ake samu a fannin kula da lafiya na ƙasar.

Sauran fannonin da sabuwar gwamnatin za ta fi bai wa fifiko sun haɗar da haɓaka damar samun ayyukan kula da lafiya ga kowa da kowa da shigar da al’umma cikin shirin inshorar lafiya na ƙasa da aƙalla kashi 40% don tabbatar da ganin duk ‘yan Najeriya ciki har da rukunin al’umma masu ƙaramin ƙarfi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?