Har Yanzu Ba a Cimma Matsaya Ba Game da Tallafin Man Fetur

Gwamnatin Tarayya ta ce har yanzu ba a cim ma matsaya ba, a kan matakan da za a dauka idan an janye tallafin fetur a tsakiyar shekarar nan.

Majiyarmu ta rawaito cewa karamin Ministan tsare-tsaren kasa da kasafi, Clement Agba ya yi bayanin nan ne bayan taron ‘Yan majalisar zartarwa a jiya Laraba.

Clement Agba ya amsa tambayoyi daga wajen manema labarai a fadar shugaban kasa bayan Muhammadu Buhari ya jagoranci taron Ministocin. Ministan ya nuna kwamitin da Farfesa Yemi Osinbajo yake jagoranta ya yi kusan shekara daya yana aiki, amma dai ba a kai ga cin ma matsaya ba.

Agba ya shaida wa manema labarai cewa suna sa ran kwamitin da yake aiki da Gwamnonin jihohi zai yanke shawara kan matsayar da za a dauka.

Baya ga haka, Agba ya ce jam’iyyu da ƙungiyoyin kwadago, da kungiyoyin matasa da mata, da malaman addini da sarakuna duk suna da ta-cewa.

Post masu alaƙa

An yi garkuwa da ɗalibai a hanyar zuwa jarrabawar JAMB

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000