Home » Hukumar Kashe Gobara ta Gargadi Mazauna Jihar Kaduna

Hukumar Kashe Gobara ta Gargadi Mazauna Jihar Kaduna

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Hukumar Kashe Gobara ta gargadi mazauna jihar Kaduna

Hukumar Kashe Gobara ta ƙasa reshen jihar Kaduna ta gargadi mazauna jihar saboda yuwuwar samun gobara a lokacin sauyin da ake dab da shiga.

Kwamandan hukumar, Sadiq Usman, wanda ya bayyana hakan a matsayin wani mataki na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya ce ya zama dole a yi wannan gargaɗi idan aka yi la’akari da yadda ake cigaba da fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Kuma a lokutan sanyi, al’umma na ninƙa yadda suke amfani da na’urori ko ma kunna wuta domin ɗumama ɗakunansu wanda hakan ke yawan haifar da gobara.

Inda ya ce suna wannan kira ne domin sauke nauyin da ke kansu wajen hana afkuwar gobara a lokacin sanyi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?