India: Wasu Mata Sun Yi Zanga-zangar Kin Amincewa da Gina Matatar Man Fatur a Kauyensu

Ɗaruruwan mata a jihar Maharashtra da ke yammacin Indiya, sun gudanar da zangazangar nuna ƙin amuncewa gwaje-gwaje da wasu jami’ai ke yi a yunƙurin gina wata katafariyar matatar man fetur a yankin.

Mata da dama ne suka zaɓi aske gashin kansu, wasu kuma suka yi yajin cin abinci, a wani mataki na nuna adawa da ƙudurin kafa matatar man.

‘Yan sanda sun sanya dokar hana zirga-zirga tare da amfani da kulake da hayaƙi mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar.

Haka zalika sun kama tare da tsare wasu mata ‘yan gwagwarmayar nuna adawa da gina matatar.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro