Mutum biyu sun rasa rayukansu bayan da wata tifa ta murƙushe babur ɗin haya da suke kai a Mahaɗar Infant Jesus da ke kan titin Rukuba, a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa da ke Jihar Filato.
Da yammacin ranar Laraba ne lamarin ya faru a daidai lokacin da mazauna yankin ke komawa gidajensu bayan kammala harkokin yau da kullum.
Wata ganau mai suna Joy Nankin ta shaida wa wakilinmu cewa direban babur ɗin hayar yana ɗauke da fasinjoji biyu ne lokacin da tifar da ke gudun wuce kima ta buge babur ɗin a mahadar.
Ta ce, “Lamarin ya faru cikin ƙanƙanin lokaci. Direban babur yana ƙoƙarin tsallaka mahadar ne sai tifar ta zo daga baya ta take su.”
Koyi ta ce a nan take mutum ɗaya ya rasu, yayin da aka garzaya da ɗayan zuwa asibiti, amma daga bisani shi ma ya rasu sakamakon raunukan da ya samu.
Shi ma wani mazaunin yankin, Jude Bako, wanda ya isa wurin jim kaɗan bayan aukuwar haɗarin, ya nuna alhininsa kan yawaitar irin waɗannan munanan haɗurra a kan titin Rukuba.
Ya ce, “Abin takaici ne matuƙa. Mun rasa rayukan mutum biyu tsaka da rana. Irin waɗannan haɗurra sun yi yawa a wannan titin.”
Lamarin ya sa mazauna yankin suka buƙaci Gwamnatin Jihar Filato da hukumomin kula da zirga-zirga su ɗauki matakan gaggawa domin inganta tsaron masu amfani da titin.
Sun roƙi gwamnati da ta faɗaɗa titin Rukuba tare da sanya tuddan rage gudu a kusa da mahadar Infant Jesus domin daƙile tukin ganganci na direbobin tifa da sauran manyan motoci.
Wani mazaunin yankin ya ce, “Ya kamata gwamnati ta faɗaɗa wannan hanya ko kuma aƙalla ta sanya tuddan rage gudu. Direbobin tipa suna tuƙi kamar babu mutane da ke zaune a wannan yanki.”
Titin Rukuba na ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da ke haɗa Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa da wasu sassan Ƙaramar Hukumar Bassa, kuma motocin kasuwanci da manyan motoci masu ɗaukar kayan gini na yawan amfani da shi.
Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, an kai gawarwakin mamatan ɗakin ajiyar gawa, yayin da jami’an tsaro ke kula da zirga-zirga a wurin domin rage cunkoso.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) a Jihar Filato, Peter Longsan, da na ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, bai yi nasara ba.