• Home  
  • INEC Ta Ayyana Zaɓen Jihar Adamawa a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba
- Siyasa

INEC Ta Ayyana Zaɓen Jihar Adamawa a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba

INEC Ta Ayyana Zaɓen Jihar Adamawa a Matsayin Wanda Bai Kammala Ba

Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyana zaben gwamnan jihar Adamawa a matsayin wanda bai kammala ba, watau “Inconclusive.”

Jami’in hukumar ta INEC wanda ke da alhakin tattara sakamakon zabe a jihar ya ce adadin katin zabe na dindindin da mutane suka karba a yankunan da aka samu matsala 37,000 ya zarce tazarar da ke tsakani.

A cewarsa, adadin ya zarce tazarar da ke tsakanin gwamna Ahmadu Fintiri na PDP da babbar abokiyar karawarsa, Sanata Aishatu Binani, ta jam’iyyar APC, kamar yadda majiyarmu ta rawaito.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000