Jami’ar Yusuf Maitama Sule Zata Karrama Aminu Dantata, Ahmad Bamba, Rabi’u Kwankwaso Da Wasu Fitattun Mutane

Shugaban Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Jihar Kano, Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, ya bayyana cewa jami’ar ta yanke shawarar karrama marigayi Sheikh Ahmad Bamba sakamakon gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jami’ar tun kafin rasuwarsa.

Farfesa Kurawa ya bayyana hakan ne a wata zantawa da ya yi da manema labarai, inda ya ce wannan karramawa wata alama ce ta girmamawa ga marigayin bisa irin rawar da ya taka.

Taron karramawar zai gudana ne a ranar Asabar, 26 ga watan Yuli, a sabon dakin taro na Convocation Arena da ke cikin harabar jami’ar.

Sauran fitattun mutanen da za a karrama sun haɗa da tsohon gwamnan Jihar Kano, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata, Hajiya Mariya Sunusi Ɗantata, da kuma wasu mutane biyu

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda