• Home  
  • An ayyana harshen Hausa cikin harsunan da za a fassara hudubar ranar Arafat
- Labarai

An ayyana harshen Hausa cikin harsunan da za a fassara hudubar ranar Arafat

Mahukunta Masallatan Alfarma na kasar Saudiyya, sun sanya Hausa a cikin jerin harsuna 20 da za a yi amfani da su wajen fassara hudubar ranar Arafa ta bana. Daidai lokacin da mahajjata a sassan duniya suka fara aikin sauke farali na bana a kasar mai tsarki.

An ayyana harshen Hausa cikin harsunan da za a fassara hudubar ranar Arafat

Mahukunta Masallatan Alfarma na kasar Saudiyya, sun sanya Hausa a cikin jerin harsuna 20 da za a yi amfani da su wajen fassara hudubar ranar Arafa ta bana. Daidai lokacin da mahajjata a sassan duniya suka fara aikin sauke farali na bana a kasar mai tsarki.

A shekarun bayan nan dai an rika fassara hudubar ranar Arafa cikin harsuna daban-daban, inda kusan shekaru uku da suka gabata harshen hausa ya samu shiga.

A wannan Lahadin ne ake soma aikin hajjin a Makkatul Mukarrama cikin yanayin zafi, inda dubun dubatar musulmi suka halarci aikin hajjin farko da aka baiwa kowa dama a masarautar tun bayan barkewar cutar Covid-19.

Sama da mahajjata miliyan biyu daga kasashe 160 ne ake sa ran zasu gudanar da Ibadan na bana a birnin mafi tsarki ga addinin musulunc a yammacin Saudiya, bayan shafe shekaru uku ana takaita adadin masu halarta saboda barkewar annobar korona.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai