Kano: An gurfanar da wani mutum a gaban kotu bisa laifin yin basaja a matsayin lauya

A Kano, an gurfanar da wani lauyan bogi mai suna Zaharaddin Sani Maidoki a gaban kotun shari’ar Musulunci bisa zargin yaudara da cin amana.

Wanda ake zargin dan asalin jihar Kaduna ne ya bayyana kansa a matsayin lauya da niyyar kare wasu mutane a gaban kotu

Zaharaddin ya amsa dukkan tuhume-tuhumen da ake zarginsa da su wanda ya hada da yin basaja a matsayin dan jarida daga jihar Kaduna.

Kotun da ke zamanta a karamar hukumar Kiru da ke jihar Kano ta daure karkashin jagorancin alkalin kotun, Abdulmuminu Nuhu wanda ya daure wanda ake zargin watanni 15 a gidan gyaran hali.

Hukuncin da Alkalin kotun ya yanke bai ba da damar biyan kudin tara ba, amma zai biya N20,000.

A yayin yanke wannan hukunci dai, kotun ta yi amfani da dokokin shari’a addinin musulinci ta jihar Kano karkashin sashe na 337 wajen yanke wancan hukunci.

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro