Kano: Hukumar Hisba ta samu wasu masu neman auren gata da cututtuka

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce an samu wasu dake ɗauke da cututtuka a cikin waɗanda ke neman a yi musu auren gata.

Mai magana da yawun  hukumar ta Hisbah, Lawan Fagge ya ce an gano wannan ne daga gwaje-gwajen da aka yi kafin auren.

Karanta Wannan: Kano: INEC ta janye ƙarar da ta ɗaukaka kan hukuncin kotu

Malam Lawan Fagge ya ce tuni an maye guraben wadannan mutane da wasu daban. Kuma hukumar Hisbah za ta taimaka wa waɗanda ke ɗauke da cututtukan da magunguna.

Kakakin na Hisbah ya kuma ce sun tantance masu neman aure kusan 5000, gwamnatin Abba Kabir Yusuf za ta aurar da mutane 1800.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr