Kano: Hukumar KAROTA za ta fara kama yara masu tuka baburan a-daidaita-sahu

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano, KAROTA, za ta ci gaba da kama yara masu tuƙa baburan a-daidaita-sahu waɗanda ba su kai shekara 18 ba.

Shugaban Hukumar KAROTA Injiniya Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka, a lokacin da yake karbar baƙuncin gamayyar ƙungiyoyin a-daidaita-sahu na jihar nan, a ƙarƙashin jagorancin Alhaji Mansur Tanimu

Injiniya Faisal ya ce Hukumar KAROTA ba za ta amince da bai wa ƙananan yaran da ba su kai shekara 18 tuƙin a-daidaita-sahu ba.

Sannan, Hukumar ta ce ba za ta yarda da yin amfani da waya a lokacin tuƙi ba, da kuma ɗaukar kaya fiye da kima a cikin a-daidaita-sahu

Sai dai gamayyar wasu ƙungiyoyi a Kano sun roƙi gwamnatin jihar da ta samar da makarantar da  za ta bayar da horo ga matuƙa a-daidaita- sahun faɗin jihar nan, domin hakan zai taimaka wajen rage aikata laifukan tuƙin da ake gani a kan titunan jihar nan.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr