Kasashen Mali, Burkina Faso, Nijar sun fice daga ECOWAS

Ƙasar Mali a maimakon ƙasashen Burkina Faso da Nijar, ta rubuta wa ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma, wato ECOWAS, takardar sanarwa na ficewa daga ƙungiyar nan take.

ƙasashen sun zargi ƙungiyar da sauka daga manufofin da suka assasa kafa ƙungiyar waɗanda ke ƙunshe da aƙidar bunƙasa yankin Afirka.


Sannan sun zargi ECOWAS da mara wa manufofin Turawan Yamma baya wanda kuma hakan barazana ne ga ƙasashen biyu a cewar takardar sanarwar.

Wannan mataki na nuna yankewar alaƙar ƙasashen na shekaru 49 tun bayan kafa ƙungiyar a ranar 28 ga watan Mayun shekarar 1975.

Post masu alaƙa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China

Babandede Ya Taya Shettima Murnar Sake Samun Takarar Mataimakin Shugaban Kasa