Katsina: ‘ya’yan ƙungiyar ƙwadago sun tsunduma yajin aiki

Wasu al’ummar cikin birnin Katsina, Sun bayyana yunkurin kungiyoyin kwadago na NLC da TUC a matsayin abu marar dalili da kuma rashin tausayin da al’umma suke ciki.

Sun bayyana cewa lamarin da ya shafi shugaban kungiyar kwadago a jihar Imo, wanda kungiyoyin kwadagon suka fake dashi abune da ya shafeshi shi kadai, inda suka bayyana cewa bai kamata a ingiza maaikata shiga yajin aikin ba, wanda yin hakan zai kara jefa rayukansu cikin mawuyacin hali.

Post masu alaƙa

Rundunar yan sandan shiyya ta daya ta kama Mutane biyar kan zargin jabun magunguna da sojan Gona.

Kwalejin sojan ruwa dake Dawakin-Tofa ta kara karfafa hadin gwiwar aiki tare da rundunar yan sandan Kano.

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.