Kotun daukaka kara ta yi watsi da karar da gwamnan Kano ya shigar gabanta

Kotun daukaka kara, dake babban birnin tarayya Abuja ta kori karar da Abba Kabir Yusuf ya shigar na neman a yi watsi da hukuncin kotun Sauraren kararrakin zaben karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay da ta zartar a ranar 13 ga Yuli, 2023.

Kotun ta yanke hukuncin ne a yau Alhamis, bayan ta bayyana karar da gwamnan Kano ya shigar a kan APC da wasu mutane 2 a matsayin “marar tushe, wadda da kuma ta cancanci a hukuncin kora”.

Izuwa yanzu dai ana daƙon ƙarin bayani game da wannan mataki da kotun ta ɗauka a kan wannan shari’a.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr