Kowa sai ya sabunta lasisinsa a Kannywood ~Abba Al-Mustapha

Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano, ta ce ta kwace lasisin gudanar duk wasu ‘yan wasa da jarumai ciki har da daraktoci, gidajen gala da masu tallan maganun-uwan gargajiya a masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood.

Shugaban hukumar, Abba Al-Mustapha ya bayyana cewa an dauki wannan matakin ne da nufin tsaftace masana’antar da kuma tabbatar da duk wanda ke ci-kin na bin ka’ida.

Al-Mustapha ya ce dole ne dukkan fitattun jarumai da furodusoshi su sabunta la-sisin yin aiki a masana’antar da hukumar tace fina-fanai ta Jihar Kano, domin kyau-tata sana’ar da kuma kauce wa gurbatattun da ke zubar da kimar sana’ar.

Sai dai kuma wannan matsayi na Al-Mustapha ya jawo suka daga mutane da da-ma, musamman ‘yan adawa wadanda suke ganin ana so a yi amfani da siyasa ne kawai domin musguna wa wasu ‘yan fim da ba su goyi bayan gwamnati mai ci ba.

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro