Kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya ta nemi a janye takunkumin da aka sa wa Nijar

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya, Arewa Consultative Forum, ta yi kira ga gwamnatin tararraya da ta cire takunkuman da ta sanyawa Nijar, sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a ƙasar.

A makon jiya ƙungiyar ta ACF ta soki batun aiki da ƙarfin soji da kungiyar Ecowas din ta ce za ta yi idan sauran matakai sun gagara.

Dattawan sun kuma yaba wa ƴan majalisar dokokin Najeriyar da suka yi watsi da maganar aikewa da karfin sojin.

A wa ni labarin, rahotanni daga jihar sokoto na nuni da cewar, Takunkumin da ƙungiyar ta Ecowas ta ƙaƙaba wa Nijar ya haifar da tashin farashin kayan abinci a kasar, wanda kuma ya shafi wasu jihohi a nan gida Najeria.

Mazauna jihar Sokoto da ke maƙwabta da Nijar sun koka kan yadda farashin shinkafa ya ke hauhawa.

Post masu alaƙa

Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka

Kotun majistare ta fara sauraren shari’ar sojan gona mai mukamin CSP 

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wanda ake zargi da damfarar mutane da cewa shi babban jami’in Dan sandan ne.