Shugaban Najeriya ya yaba wa Farfesa Ali Pate bisa kwazon da ya nuna a majalisa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yaba wa Farfesa Ali Pate, ɗaya daga cikin ministocin da majalisr dattawa ta amince da su, bisa kwazon da ya nuna a lokacin da ake tantance shi a majalisar.

Farfesa Pate ya taɓa riƙe muƙamin ƙaramin ministan lafiya a ƙarƙashin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan.

Kafin a naɗa shi ya zama minista, Pate ya yi murabus daga shugabancin kamfanin ‘GAVI- Global Alliance for Vaccines and Immunization’ inda ya yi nuni da cewa zai samu muƙami a gwamnatin Shugaba Tinubu.

A jiya Talata, 8 ga watan da muke ciki, Pate ya raka Ngozi Okonjo-Iweala, Darekta Janar ta ƙungiyar kasuwanci ta duniya domin ziyartar Shugaba Tinubu a fadarsa.

Shugaba Tinubu ya gaya masa cewa ya kalli yadda tantancewar ta sa ta kasance a talbijin ya kuma yaba masa da irin ƙwazon da ya nuna a wajan.

Post masu alaƙa

Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka

Kotun majistare ta fara sauraren shari’ar sojan gona mai mukamin CSP 

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wanda ake zargi da damfarar mutane da cewa shi babban jami’in Dan sandan ne.