Shugaban Najeriya ya yaba wa Farfesa Ali Pate bisa kwazon da ya nuna a majalisa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yaba wa Farfesa Ali Pate, ɗaya daga cikin ministocin da majalisr dattawa ta amince da su, bisa kwazon da ya nuna a lokacin da ake tantance shi a majalisar.

Farfesa Pate ya taɓa riƙe muƙamin ƙaramin ministan lafiya a ƙarƙashin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan.

Kafin a naɗa shi ya zama minista, Pate ya yi murabus daga shugabancin kamfanin ‘GAVI- Global Alliance for Vaccines and Immunization’ inda ya yi nuni da cewa zai samu muƙami a gwamnatin Shugaba Tinubu.

A jiya Talata, 8 ga watan da muke ciki, Pate ya raka Ngozi Okonjo-Iweala, Darekta Janar ta ƙungiyar kasuwanci ta duniya domin ziyartar Shugaba Tinubu a fadarsa.

Shugaba Tinubu ya gaya masa cewa ya kalli yadda tantancewar ta sa ta kasance a talbijin ya kuma yaba masa da irin ƙwazon da ya nuna a wajan.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.

Kwamitin yaki da shaye-shaye da fadan daba na Kano ya nemi hadin kan hukumomin tsaro