Kungiyar direbobi masu dakon man fetur sun fara yajin aiki a Kasar Ghana

Kungiyar direbobin tankokin dakon man fetur a Ghana ta ce za ta fara yajin aiki a yau Litinin saboda rashin kyawun hanyoyi.

Direbobin na so ne gwamnati ta gyara hanyoyi a yankunan Tema, Takoradi da Buipe.

Sun nuna damuwa kan hadurran da ke tattare da safarar man fetur a kan hanyoyin marasa kyau.

Kungiyar yan kasuwa ta Liquified Petroleum Gas Marketers Association ta yi gargadin cewa za a iya samun karancin man LPG a kasar idan har aka shiga yajin aikin.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM