Kungiyar direbobi masu dakon man fetur sun fara yajin aiki a Kasar Ghana

Kungiyar direbobin tankokin dakon man fetur a Ghana ta ce za ta fara yajin aiki a yau Litinin saboda rashin kyawun hanyoyi.

Direbobin na so ne gwamnati ta gyara hanyoyi a yankunan Tema, Takoradi da Buipe.

Sun nuna damuwa kan hadurran da ke tattare da safarar man fetur a kan hanyoyin marasa kyau.

Kungiyar yan kasuwa ta Liquified Petroleum Gas Marketers Association ta yi gargadin cewa za a iya samun karancin man LPG a kasar idan har aka shiga yajin aikin.

Post masu alaƙa

Barista Hamza Ɗantani ya jinjinawa CP Bakori da wasu kwamishinonin yan sanda biyu.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ceto fasinjoji 9 bayan musayar wuta da yan bindiga a hanyar Doguwa.

Kwalejin Fasaha ta Kogi ta dakatar da lakcarori 7 kan cin zarafin ɗalibai