Kasashen Ketare

Shettima ya tafi Angola domin wakiltar Tinubu a taron AU

Mataimakin Shugaban Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya tashi daga Abuja zuwa Luanda babban birnin Angola, domin wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron shugabannin ƙasashen Tarayyar Afirka (AU) na musamman karo na 21. Sanarwar da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, ya fitar ta ce taron zai mayar da hankali kan hanyoyin […]

Read more

‘An koma haƙo man fetur a yankin Kurdistan na Iraq’

Ministan Albarkatun Ƙasar Iraq, Kamal Mohammed, ya bayyana cewa an koma haƙo man fetur a yankin Kurdistan bayan hare-haren jiragen sama marasa matuƙa da suka kai wa wasu filayen mai da cibiyoyin samar da shi hari. Ya ce kamfanonin mai sun koma aiki, kuma yawan man da ake haƙowa a yankin ya kai tsakanin ganga […]

Read more

Sakataren sojin kasan Amurka zai yi murabus

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga Mujallar Wall Street cewa ana sa ran Sakataren Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka, Dan Driscoll, zai yi murabus kafin ƙarshen shekara, bayan watanni ana samun takun-saka tsakaninsa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth. Mujallar Wall Street Journal ta wallafa rahoton ne bisa bayanan wasu mutane da ke […]

Read more

Yadda Ebola ke mayar da yara marayu a Kwango

Wani sabon rahoton da ƙungiyar kula da yara ta Save the Children ta fitar ya ce aƙalla yara 180 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango ne suka rasa uwa da uba ko kuma ɗaukacin masu kula da su sanadiyyar ɓarkewar cutar Ebola tun daga watan Mayu. Hukumomi a lardin Ituri, inda nan ne cibiyar yaɗuwar cutar sun […]

Read more

Iran ta ƙera jirgi mara matuƙi mai layar zana

Iran ta ƙera wani sabon jirgi mara matuƙi mai suna Hadid 110, wanda aka ce yana tafiya da matsanancin sauri a ƙasa ƙasa, wanda ke iya kai farmaki cikin gaggawa kamar layar zana kafin na’urorin kariyar sararin samaniya su gano shi.  Jaridar The Telegraph ta Birtaniya ta rawaito cewa jirgin na iya yin gudun sama […]

Read more