Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano CP Ibrahim Adamu Bakori ya raba tallafin ₦8,431,768.80 ga iyalan yan sandan da suka rasu.

Rundunar ‘ƴan sandan Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin , CP Ibrahim Adamu Bakori,  ta raba Cek ɗin kuɗi Naira miliyan takwas da dubu ɗari 431 da 768 da kobo 80 (₦8,431,768.80) ga iyalan jami’an rundunar 18 da suka rasu.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar CSP Abdullahhi Haruna Kiyawa, ya bayyana ta cikin wata sanarwa da rabawa manema labarai.

Sanarwar ta ce wannan wani ɓangare ne na bikin ranar ƴan sanda ta shekarar 2026, a tsarin tallafin babban sufeton ƴan sandan Nijeriya GP Olatunji Rilwan Disu, don kula da walwalar ƴan sanda da iyalansu musamman waɗanda sukaji rauni ko kuma suka rasu a bakin aiki.

CP Bakori ya shawarci waɗanda suka amfana da tallafin su yi amfani dashi yadda ya dace, tare da yin addu’a ga mamatan.

Anasu ɓangaren waɗanda suka samu tallafin sun bayyana godiyarsu da kuma farin cikin kan yadda rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta jajirce wajen kula da rayuwarsu.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda