Kwamishinan ‘yan sandan Kano zai ba da tukuicin dubu 300 domin kama wasu ‘yan daba

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sanya tukuicin naira dubu ɗari uku ga duk wanda ya ba wa hukumar bayani game da wasu ‘yan daba da take nema ruwa a jallo.

Wannan na zuwa ne a wani  ɓangare na cigaba da yaƙi da ayyukan daba da ƙwacen waya a jihar nan wanda kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano ya sha alwashin kawo ƙarshensa.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM