Zan tabbatar da APC ta lashe zabuka masu zuwa ~ Abdullahi Umar Ganduje

Sabon shugaban jami’iyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya ce zai kama aiki ba ji ba gani domin tabbatar da jam’iyyarsa ta yi nasara a zaɓen gwamnan jihohin Kogi da Bayelsa da za a gudanar ranar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Ganduje ya bayyana haka ne a yau Alhamis, lokacin da yake jawabi bayan tabbatar da shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC, a wajen taron majalisar zartarwar jam’iyyar da ya gudana a Abuja.

An kuma zaɓi tsohon mai magana da yawun Majalisar Dattijan Najeriya, Ajibola Basiru, ɗan jihar Osun a matsayin sakataren Jam’iyar.

A jawabin nasa, Ganduje ya gode wa Shugaba Bola Tinubu, ya kuma jaddada cewa zai tabbatar da zaman lafiyar a cikin jam’iyar.

Ganduje ya yi alƙawarin yin aiki tuƙuru wajen tabbatar da nasarar jam’iyar a zaɓen gwamnan jihar Kogi da Imo da Bayelsa

Post masu alaƙa

An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi a Kano

APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano

Bukatunmu kan gyaran dokar zaɓen Najeriya – El-Rufai