A shirye-shiryen bude sashen talabijin na Muhasa baya ga sashen rediyo da tuni ya daɗe da fara aiki kan mita 92.3 a zangon FM, wasu daga cikin ma’aikatan wannan gida sun samu horo na musanman na sannin makamar aiki a bangaren talabijin.
Wannan wani mataki ne tabbatar da an samu ƙwarewa da kuma gabatar da ingantattun ayyuka ga al’ummar da ake yi dominsu.